Tunda muke wallahi ka cire son rai da son zuchiya bamu taba sanatan da yake son Al,umar sa kuma yake kaunar Al,umma tasa tare da kwatanta musu Sosai kamar Sen Ahmad Abdulhamid .
Amman abun mamaki, wai sai gashi da dama daga acikin Al,Ummar na kalubalantar alkhairin da yake saboda basu akama ba. Mu kuwa Muna hangen koda ba Kai akama abuba idan aka ma Al,Uma kaima an Maka tunda duk tare zaku amfana
kaduba Dan karamin musali lokachin da wutar lantarki din birniwa , Guri da kirikasamma ta samu matsala, barayi suka yanke mana wayar wutar a kalla mun Kai wata uku babu wutar a wannan yankunan babu Kuma labarin gyaran ta . Ta zauna Yanke , sai wannan bawan Allah ya bada Aikin gyarawa . Haka satar da akayi na wayar na farko ma shine ya gyara. Karku manta Kuma muna da Yan majalissun jaha a wannan yankunan guda uku Kuma muna da Yan majalissun tarayya da chiyamomi ko su kujerar su bata taimakon Al,Uma bace da bazasu taimaka su gyara ba
Me yasa komai ya tashi ko a jam’iya ko Kuma a garuruwan hadejia Emirate ba,a tunkarar kowa sai amb Ahmad Abdulhamid malam madori shi Kuma baya duba kowa, saboda kaunar Al, Umarsa, Amman babu abun zagi a wurin mutane sama dashi
ya kamata mu zama masu furta alkhairi ga Wanda yayi alkhairi ubangiji Allah ya Saka Maka da alkairi sen Ahmad Abdulhamid malam madori, Muna Jin dadin abinda kake mana , Dan haka Muna maka fatan alkairi har gobe.
